Kasashe 10 Da Aka Fi Dauke Wutar Lantarki A Afirka - Android Pols - latest news, natural remedies, and entertainment

Kasashe 10 Da Aka Fi Dauke Wutar Lantarki A Afirka

Kasashe 10 Da Aka Fi Dauke Wutar Lantarki A Afirka
Kasashe 10 Da Aka Fi Dauke Wutar Lantarki A Afirka


Dauke wutar lantarki a Najeriya a shekara ya fi yawan kwanakin shekara.


Wani rahoto kan kasashen da suka fi fama da matsalar wutar lantarki a duniya ya nuna cewa a Najeriya ana dauke wuta kusan sau 400 a shekara.


Rahoton da cibiyar Utility Bidder ta kasar Birtaniya ta fitar na nuni da cewa ana dauke wutar lantarki akalla sau 394 a duk shekara a Najeriya, wanda shi ne mafi muni a Afirka.


Hakan na nufin adadin dauke wutar da ake yi a kasar a duk shekara ya haura yawan kwanakin shekarar.


Cibiyar Utility Bidder wadda ke bincike kan dauke wutar lantarki da kuma asarar da hakan ke haifarwa a bangaren masana’antu ta bayyana cewa kasa ta biyu wajen dauke wuta a Afirka ita ce Afirka ta Tsakiya (CAR), amma na Najeriya ya zarce nata sau 46.


Ga dai jerin kasashen Afirka 10 da aka fi dauke wuta a Afirka da kuma adadin dauke wutarsu a shekara:


1. Najeriya – 394

2. Afirka ta tsakiya – 349

3. Benin – 336

4. Nijar – 264

5. Congo – 258

6. Gambia – 253

7. Burundi – 199

8. Zambia – 160

9. DR Congo – 148

10. Burkina Faso – 118


Binciken ya tataro alkaluma ne daga shekarar 2014 zuwa 2022, wanda ke nuna munin matsalar na iya shan bamban da hakikanin halin da ake ciki a halin yanzu.


Rashin tsayayyiyar wutar lantarki a Najeriya ya zame mata abin gori daga makwabtanta, musamman lokacin Gasar Kofin Nahiyar Afirka (AFCON).

Related Posts:
Previous article
Next article

Leave Comments

Post a Comment

Iklan Atas Artikel

Iklan Tengah Artikel 1

Iklan Tengah Artikel 2

Iklan Bawah Artikel