Yadda Tashin Bom Ya Halaka Mutane 8, Tare Da Jikkata Da Dama A Jihar Borno

Yadda Tashin Bom Ya Halaka Mutane 8, Tare Da Jikkata Da Dama A Jihar Borno

Yadda Tashin Bom Ya Halaka Mutane 8, Tare Da Jikkata Da Dama A Jihar Borno


Yadda Tashin Bom Ya Halaka Mutane 8, Tare Da Jikkata Da Dama A Jihar Borno


Rahotanni daga jihar Borno ya tabbatar cewa akalla mutane 8 ne ake fargabar sun mutu sakamakon fashewar wasu bama-bamai a kan hanyar Ngala zuwa Dikwa a Karamar Hukumar Ngala.


Majiyar ta tabbatar cewa, mutane da dama sun samu raunuka a sakamakon tashin bom din a kauyen Kinewba a ranar Talata. Wata majiyar tsaro ta ce “Akalla Mutane  8 ne ake fargabar sun mutu, ciki har da yara biyu, sannan wasu da dama sun samu munanan raunuka sakamakon fashewar nakiyoyin.”


Majiyar ta ce fashewar bom din ya yi kaca-kaca da wasu motocin biyu yaddda ba za a iya gyara su ba.


Wata babbar majiya ta jami’an farin kaya na  JTF ta ce motocin biyu kirar Isuzu da wata babbar mota ce suka taka bom din kuma ana fargabar kashe kusan dukkan fasinjojin ciki.


“Wadannan motocin dai sun bar garin Ngala da misalin karfe 9 na safe, yayin da lamarin ya faru a nisan kilomita 15,” in ji majiyar.


Aminiya ta ruwaito cewa, tashin bama-baman ya faru ne a tazarar kilomita 15 daga Maiduguri, babban birnin jihar.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post