Mai Gadin Dake Kula Da Kabarin Manzon Allah (SAW) Ya Mutu

Mai Gadin Dake Kula Da Kabarin Manzon Allah (SAW) Ya Mutu 


Abdou Ali Idris Sheikh Mai Gadin Dake Kula Da Kabarin Manzon Allah (SAW) Ya Mutu 


Agha Abdou Ali Idris Sheikh wanda ke kula da kabarin Manzon Allah (SAW) a Masallacin madina ya rasu. Yana daga cikin mutanen da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kula da hidima a Masallacin Manzon Allah (SAW) dake garin madina. 


Agha Abdou Ali Idris Sheikh, ya rasu ne a ranar Litinin, kuma tuni aka yi jana'izar sa a Masallacin Manzon Allah sannan aka kai shi Makabartar Baki ake kusa da Masallacin madina, cewar hukumar Gudanarwa Masallatan Harami. 


Cikin shekaru 10 da suka gabata Abdou Ali Idris Sheikh shine na uku da suka mutu. A baya yawan masu aikin Agha ya haura mutum dubu daya, amma a halin yanzu wadanda suka rage a raye ba su fi biyar.


Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post