Yanzu-Yanzu: Sanata Godswill Akpabio ya lashe zaben shugaban Majalisar Dattijai ta 10 - Android Pols

 


Labari Da Dumi-Dumi na nuna cewa: Sanata Godswill Akpabio ya lashe zaben shugaban Majalisar Dattijai ta 10 a zaben da sababbin 'yan majalisar sukayi a safiyar yau Talata. 


Sanata Akpabio wanda ya fito daga jihar Akwa Ibom ya kada abokin takarar sa Sanata Abdulaziz Yari, tsohon gwamnan jihar Zamfara  da kuri'a - 63 yayin da Abdulaziz Yari ya samu kuri'a - 46. 


Sanata Barau Jibril daga jihar Kano ne mataimakin shugaban majalisar dattijan Nigeria yanzu. 


Wanne irin fata kuke yiwa sabuwar majalisar dattijan Nigeria?

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post