Labaran Duniya
Gwamnatin Jihar Kano Ta Cigaba Da Rushe Gine-Ginen Aka Yi Ba Bisa Ka'ida Ba - Android Pols
Sunday, June 4, 2023
0
A jawabin da ya gabatar a lokacin da ake rantsar dashi a matsayin gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani gini da aka yi ba bisa ka’idaba a Kano.
Tun kafin wannan lakoci ana ganin takun sakar dake tsakanin tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Gandu, Abba Kabir, zai iya daukar mataki akan gine-ginen da Ganduje ya yi.
Yanzu haka dai tini Engr. Abba Kabir Yusuf, ya fara rushe wasu daga cikin gine-ginen.
Wasu na ganin matakin rushewar a matsayin abin da bai kamataba wasu kuwa suna ganin hakan dai-dai ne .
Anaka ra’ayin ya ka kalli matakin da Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya dauka na rusau a Jihar Kano ?
Sai mun ji daga gareku.
Previous article
Next article
Leave Comments
Post a Comment