Anyi Garkuwa da wata mata a Katsina bayan ta Wallafa za ta yi tafiya a shafinta na Facebook - Android Pols - latest news, natural remedies, and entertainment

Anyi Garkuwa da wata mata a Katsina bayan ta Wallafa za ta yi tafiya a shafinta na Facebook



Wata mata mai suna Ramlat Alh Shehu Aji an yi garkuwa da ita a hanyarta ta zuwa jihar Katsina daga Kagara a karamar hukumar Rafi a jihar Neja bayan ta bayyana inda ta ke a Facebook. 


Ramlat a ranar Sabuwar Shekara, Janairu 1, 2023,  ta wallafa a shafinta na Facebook cewa tana kan hanyarta ta zuwa Funtuwa amma bata isa inda zata nufa ba. 


Kawar ta , Aisha Nasafe ta tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka sace ta a Birnin Gwari, Kaduna. 


Wani da ya wallafa labarin a shafinsa na Facebook Alhaji Abdullahi Dan Gaske ya bayyana cewa yanzu tilas ne mutane su Kula wajen wallafa labarin inda suke a kafafen sada zumunta. 


 Masu yin garkuwa da mutane sun yadu a ko ina a shafukan sada zumunta kuma suna ganin dukkan abubuwan da kowa yake yi, cewarsa. 


Related Posts:
Previous article
Next article

Leave Comments

Post a Comment

Iklan Atas Artikel

Iklan Tengah Artikel 1

Iklan Tengah Artikel 2

Iklan Bawah Artikel