Yadda Rikicin Boko Haram Ya Maida Miloniya Tallan Ruwa - Android Pols - latest news, natural remedies, and entertainment

Yadda Rikicin Boko Haram Ya Maida Miloniya Tallan Ruwa


Malam Isa Ibrahim wani hamshakin mai kudi ne da ya shahara a fagen noma a garin Baga dake jihar Borno kafin fitowar 'yan Boko Haram. 


Malam Isa Ibrahim, mai shekaru 67 yana noma Albasa sama da Buhu 100 da Masara sama da Buhu 100, yana samun akalla riban Miloyan biyu cikin kowacce Shekara. Sai dai  rikicin Boko Haram ya tilasta masa tserewa daga garin Baga ba tare da ya dauki ko sisin kobo daga dukiyar sa ba a shekarar 2014.


Yanzu haka Malam Isa ya koma tura kurar Ruwa inda yake samun abunda zai sanya a bakin Salati.


Tun bayan fara ayyukan Boko Haram dubban mutane ne a arewa maso gabas suka rasa gidajen su da matsugunan su. 

Related Posts:
Previous article
Next article

Leave Comments

Post a Comment

Iklan Atas Artikel

Iklan Tengah Artikel 1

Iklan Tengah Artikel 2

Iklan Bawah Artikel