Hoton 'yan matan Chibok uku da aka sake kubutarwa a hannun 'yan Boko Haram a ranar Juma'a - Android Pols - latest news, natural remedies, and entertainment

Hoton 'yan matan Chibok uku da aka sake kubutarwa a hannun 'yan Boko Haram a ranar Juma'a


Rudunar Sojin Hadin Guiwa ta 'Operation Hadin Kai' ce ta yi nasarar kubutar da 'yan matan tare da 'ya'yansu a Jihar Borno.


A watan da ya gabata ma sojoji Sun kubutar da wasu daga cikin daliban makarantar sakandiren ta chibok a garin bama su 2 dauke da 'ya'yan su. 


A baya-bayan nan dai kungiyar 'yan tada kayar baya na Boko Haram da ISWAP suna fuskantar matsi daga wajen sojojin Najeriya inda ake yawan kai musu hare-hare a maboyar su wanda ke sanadin mutuwar su da kuma guduwa daga maboyar su. 


Dama dai gwamnatin Najeriya ta bada umarni ga rundunar tsaro da su yi gaggawar kawo karshen ayyukan 'yan ta'adda A fadin kasar kafin zuwa Karshen Disamba na 2022. 


Hoto: Hassan Ibrahim

Related Posts:
Previous article
Next article

Leave Comments

Post a Comment

Iklan Atas Artikel

Iklan Tengah Artikel 1

Iklan Tengah Artikel 2

Iklan Bawah Artikel