Breaking News
DOKA: Idan Ba Kada Sama Da Naira Miliyan 5 Ba Za Ka Yi Aure A Jihar Rivers Ba
Tuesday, July 26, 2022
0
Gwamnatin Jihar Rivers karkashin jagorancin Nyesom Wike ta kafa wata kungiya inda ta dauki matasa dubu 10 a matsayin Kwamitin kula da sha'anin gudanar da aure a jihar.
An kafa kungiyar ne domin tabbatar da cewa duk wani namiji a jihar da yake son yai aure to dole ya sai yana da a kalla Naira Miliyan 5 ko kuma wata kadara wacce take kwatankwacin adadin miliyan 5.
Jaridar Express Express Nigeria itace ta wallafa labarin a shafinta na Facebook, sai dai ba su bayyana shin dokar ta fara yin aiki ne ko kuma ba ta fara ba. Nan gaba za muyi bincike don kawo muku sharhi akai.
Previous article
Next article
Leave Comments
Post a Comment