Breaking News
Mayaƙan ISWAP Fiye Da 300 Ne Suka Ajiye makaman Su Tare Da Miƙa Wuya Ga Rundunar Sojin Najeriya
Thursday, June 30, 2022
0
A cigaba da ayyukan da rundunar sojin Najeriya suke yi na dakile ayyukan ƴan bindiga a yankin arewa maso gabas, wannan makon ma sunyi wata nasara a ayyukan nasu inda wasu mayaƙan ISWAP suka miƙa wuya.
Rundunar sojin a wata sanarwa da ta fitar a shafin ta na facebook a ranar 29 ga watan June na shekarar 2022 ta bayyana cewa ta samu wata gagarumar nasara a jihar Borno.
A sanarwar tace kimanin mayaƙan ISWAP su 314 ne suka ajiye makaman su tare da miƙa wuya ga rundunar sojin a karamar hukumar Bama ta Jihar.
Baya ga haka kuma hukumar ta sanar da cewa ta kuɓutar da wasu manoma kimanin su 12 da aka yi ƙoƙarin yin garkuwa dasu.
Previous article
Next article
Leave Comments
Post a Comment